{"id":160570,"date":"2026-09-06T13:53:13","date_gmt":"2026-09-06T13:53:13","guid":{"rendered":"https:\/\/www.europesays.com\/dk\/160570\/"},"modified":"2026-09-06T13:53:13","modified_gmt":"2026-09-06T13:53:13","slug":"najeriya-ta-yi-rashi-babban-jamiin-dan-sanda-ya-riga-mu-gidan-gaskiya","status":"publish","type":"post","link":"https:\/\/www.europesays.com\/dk\/160570\/","title":{"rendered":"Najeriya Ta Yi Rashi: Babban Jami&#8217;in Dan Sanda Ya Riga Mu Gidan Gaskiya"},"content":{"rendered":"<p>        Rundunar &#8216;yan sandan Najeriya ta yi rashi na daya daga cikin manyan jami&#8217;an da take da su a jihar Zamfara da ke yankin Arewa maso YammaMataimakin kwamishinan \u2019yan sanda na Zamfara mai kula da ayyuka, DCP Asbagu Aliyu Muhammad, ya rasu da misalin \u0199arfe 1:30 na dareDCP Muhammad ya rasu ne a Asibitin Kwararru na Ahmed Sani Yariman Bakura da ke Gusau, bayan ya yi jinya<\/p>\n<p class=\"align-left\">\u200b\u200b\u200b\u200b\u200b\u200b\u200b\u200b\u200b\u200b\u200b\u200b\u200b\u200bEditan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al&#8217;amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi <\/p>\n<p class=\"align-left\">Jihar <a href=\"https:\/\/www.legit.ng\/tags\/zamfara-state-news-today\/\" rel=\"noopener nofollow\" target=\"_blank\">Zamfara<\/a> &#8211; Mataimakin Kwamishinan \u2019Yan Sanda (DCP) mai kula da ayyuka a rundunar \u2019yan sandan Jihar Zamfara, Asbagu Aliyu Muhammad, ya rasu.<\/p>\n<p class=\"align-left\">DCP Muhammad ya rasu ne da misalin \u0199arfe 1:30 na dare a Asibitin Kwararru na Ahmed Sani Yariman Bakura da ke Gusau.<\/p>\n<p><img class=\"article-image__picture\"  src=\"https:\/\/www.europesays.com\/dk\/wp-content\/uploads\/2026\/09\/33a269e0fa8eb27b.jpeg\"  alt=\"Mataimakin kwamishinan 'yan sanda a Zamfara ya rasu\" title=\"Mataimakin kwamishinan 'yan sanda a Zamfara ya rasu\" width=\"1120\" height=\"630\" decoding=\"async\" fetchpriority=\"high\"\/>Mataimakin kwamishinan &#8216;yan sanda a Zamfara, marigayi DCP Asbagu Aliyu Muhammad<br \/>Source: Facebook<\/p>\n<p class=\"align-left\">Ya rasu bayan jinya Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kakakin rundunar \u2019yan sandan Zamfara, DSP Yazid Abubakar, ya fitar, wadda Legit <a href=\"https:\/\/hausa.legit.ng\/\" rel=\"nofollow noopener\" target=\"_blank\">Hausa<\/a> ta samu.<\/p>\n<p><a href=\"https:\/\/hausa.legit.ng\/siyasa\/1729079-zaben-2027-adc-ta-fitar-da-jerin-sunayen-yan-takararta-na-gwamna-a-jihohi-28\/\" class=\"c-article-read-also__image-wrapper\" rel=\"nofollow noopener\" target=\"_blank\"><img src=\"https:\/\/www.europesays.com\/dk\/wp-content\/uploads\/2026\/09\/a31f965f98997cc5.jpeg\"   loading=\"lazy\" decoding=\"async\"\/><\/a><a href=\"https:\/\/hausa.legit.ng\/siyasa\/1729079-zaben-2027-adc-ta-fitar-da-jerin-sunayen-yan-takararta-na-gwamna-a-jihohi-28\/\" class=\"c-article-read-also__headline\" rel=\"nofollow noopener\" target=\"_blank\"><\/p>\n<p class=\"c-article-read-also__caption\">Kara karanta wannan<\/p>\n<p class=\"c-article-read-also__headline-wrapper\">Zaben 2027: ADC ta fitar da sunayen &#8216;yan takararta na gwamna a jihohi 28<\/p>\n<p><\/a><\/p>\n<p class=\"align-left\">A cewar sanarwar da kakakin ya fitar, marigayin yana jinya ne sakamakon wata rashin lafiya da ba a bayyana sunanta ba.<\/p>\n<p class=\"align-left\">Sanarwar ta bayyana marigayin a matsayin babban jami\u2019in \u2019yan sanda wanda ya yi wa Rundunar \u2019Yan Sandan Najeriya hidima cikin sadaukarwa, \u0199warewa da kuma jajircewa wajen gudanar da aikinsa.<\/p>\n<p>Rundunar ta bayyana rasuwar a matsayin babban rashi<\/p>\n<p class=\"align-left\">Rundunar ta ce rasuwar DCP Muhammad babban rashi ne ga Rundunar \u2019Yan Sandan Jihar Zamfara, abokan aikinsa da kuma daukacin Rundunar \u2019Yan Sandan Najeriya.<\/p>\n<p class=\"align-left\">Kwamishinan \u2019Yan Sandan Jihar Zamfara, CP Ahmad Muhammad Bello, ya mika ta\u2019aziyyarsa ga iyalan marigayin, \u2019yan uwansa da abokan aikinsa.<\/p>\n<p class=\"align-left\">Ya ro\u0199i Allah Ma\u0257aukakin Sarki Ya gafarta wa marigayin kurakuransa, Ya kar\u0253i kyawawan ayyukansa.<\/p>\n<p>An shirya jana\u2019izarsa<\/p>\n<p class=\"align-left\">CP Bello ya kuma ro\u0199i Allah Ya ba marigayin Aljannatul Firdaus, tare da bai wa iyalansa da abokan aikinsa ha\u0199urin jure wannan babban rashi.<\/p>\n<p class=\"align-left\">An tsara gudanar da jana\u2019izar marigayin da \u0199arfe 2:00 na rana a yau, Lahadi, 6 ga watan Satumban 2026 a masallacin Sheikh Ibn Umar Kanoma, bisa tsarin jana\u2019izar Musulunci.<\/p>\n<p><a href=\"https:\/\/hausa.legit.ng\/news\/1728891-an-kama-dalolin-bogi-a-kaduna-sun-kai-naira-miliyan-30\/\" class=\"c-article-read-also__image-wrapper\" rel=\"nofollow noopener\" target=\"_blank\"><img src=\"https:\/\/www.europesays.com\/dk\/wp-content\/uploads\/2026\/09\/35473ff943a9a968.jpeg\"   loading=\"lazy\" decoding=\"async\"\/><\/a><a href=\"https:\/\/hausa.legit.ng\/news\/1728891-an-kama-dalolin-bogi-a-kaduna-sun-kai-naira-miliyan-30\/\" class=\"c-article-read-also__headline\" rel=\"nofollow noopener\" target=\"_blank\"><\/p>\n<p class=\"c-article-read-also__caption\">Kara karanta wannan<\/p>\n<p class=\"c-article-read-also__headline-wrapper\">An kama dalolin bogi na Naira miliyan 30 ana kokarin shiga da su jama&#8217;a<\/p>\n<p><\/a><\/p>\n<p class=\"align-left\">Rundunar \u2019yan sandan Zamfara ta mi\u0199a ta\u2019aziyyarta ga iyalan marigayin, tare da ro\u0199on Allah Ya sa ruhinsa ya huta cikin aminci.<\/p>\n<p><img class=\"article-image__picture\"  src=\"https:\/\/www.europesays.com\/dk\/wp-content\/uploads\/2026\/09\/b1f2e1684ed256d3.jpeg\"  alt=\"Mataimakin kwamishinan 'yan sanda a Zamfara ya rasu\" title=\"Mataimakin kwamishinan 'yan sanda a Zamfara ya rasu\" width=\"1120\" height=\"588\" decoding=\"async\" loading=\"lazy\"\/>Taswirar jihar Zamfara, tarayyar Najeriya<br \/>\nHoto: Legit.ng<br \/>Source: OriginalKaranta wasu labaran kan &#8216;yan sandaDan sanda ya yi murabus a Bauchi<\/p>\n<p class=\"align-left\">A <a href=\"https:\/\/hausa.legit.ng\/news\/1728915-dan-sanda-ya-yi-murabus-a-bauchi-ya-ce-shekaru-2-bai-samu-albashinsa-ba\/\" target=\"_blank\" rel=\"nofollow noopener\">wani labarin<\/a> kuma, kun ji cewa rundunar \u2019yan sandan <a href=\"https:\/\/www.legit.ng\/tags\/bauchi-state-news-today\/\" rel=\"noopener nofollow\" target=\"_blank\">Bauchi<\/a> ta fara bincike kan lamarin wani jami\u2019i da ya sanar da murabus, yana zargin hana shi samun albashinsa shekaru biyu. <\/p>\n<p class=\"align-left\">Jami\u2019in mai lamba F\/No. 524180, CPL Yusuf Aliyu, ya bayyana murabus \u0257insa daga rundunar \u2019yan sandan Najeriya ta kafafen sada zumunta. <\/p>\n<p class=\"align-left\">Dan sandan ya yi ikirarin cewa tsawon wannan lokaci bai samu damar cire albashin da ake biya masa ba, lamarin da ya sa ya bayyana damuwarsa. <\/p>\n<p>Asali: Legit.ng<\/p>\n","protected":false},"excerpt":{"rendered":"Rundunar &#8216;yan sandan Najeriya ta yi rashi na daya daga cikin manyan jami&#8217;an da take da su a&hellip;\n","protected":false},"author":2,"featured_media":160571,"comment_status":"","ping_status":"","sticky":false,"template":"","format":"standard","meta":{"footnotes":"","_share_on_mastodon":"0"},"categories":[91],"tags":[169,168],"class_list":["post-160570","post","type-post","status-publish","format-standard","has-post-thumbnail","category-riga","tag-latvia","tag-riga"],"share_on_mastodon":{"url":"https:\/\/pubeurope.com\/@dk\/117224433892044065","error":""},"_links":{"self":[{"href":"https:\/\/www.europesays.com\/dk\/wp-json\/wp\/v2\/posts\/160570","targetHints":{"allow":["GET"]}}],"collection":[{"href":"https:\/\/www.europesays.com\/dk\/wp-json\/wp\/v2\/posts"}],"about":[{"href":"https:\/\/www.europesays.com\/dk\/wp-json\/wp\/v2\/types\/post"}],"author":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/www.europesays.com\/dk\/wp-json\/wp\/v2\/users\/2"}],"replies":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/www.europesays.com\/dk\/wp-json\/wp\/v2\/comments?post=160570"}],"version-history":[{"count":0,"href":"https:\/\/www.europesays.com\/dk\/wp-json\/wp\/v2\/posts\/160570\/revisions"}],"wp:featuredmedia":[{"embeddable":true,"href":"https:\/\/www.europesays.com\/dk\/wp-json\/wp\/v2\/media\/160571"}],"wp:attachment":[{"href":"https:\/\/www.europesays.com\/dk\/wp-json\/wp\/v2\/media?parent=160570"}],"wp:term":[{"taxonomy":"category","embeddable":true,"href":"https:\/\/www.europesays.com\/dk\/wp-json\/wp\/v2\/categories?post=160570"},{"taxonomy":"post_tag","embeddable":true,"href":"https:\/\/www.europesays.com\/dk\/wp-json\/wp\/v2\/tags?post=160570"}],"curies":[{"name":"wp","href":"https:\/\/api.w.org\/{rel}","templated":true}]}}